SiyasaGabas ta Tsakiya
An shirya bude taron sulhun Masar kan yakin Gaza
April 28, 2024![Birnin Jabalia da dakarun Isra'ila ta shafe a Gaza](https://static.inspiredminds.de/image/68349035_800.webp)
Talla
Jami'in wanda ya nemi a sakaye sunansa ya ce kungiyar za ta isa kasar Masar a karkashin jagorancin Khalil al-Hayya, inda zai gabatar da bayanai kan bukatar da Isra'ila ta gabatar na tsagaita wuta da musayar fursunoni.
Karin bayani: Guterres: Gabas ta Tsakiya ka iya fadawa yaki
An dai shiga wata na bakwai a luguden wutan da Isra'ila ke yi a yankin Gaza da zummur murkushe mayakan Hamas da suka kai mata hari a ranar 7 ga watan Oktoba, wanda yayi sanadiyyar mutuwar al'ummar Isra'ilan 1,200.
Karin bayani: Isra'ila za ta shiga sulhun Masar bayan kashe jami'an jinkai
Hare-haren na Isra'ila na fatattakar kungiyar ta Hamas ya yi sanadiyyar mutuwar Falasdinawa sama da 34,000 a cewar ma'aikatar lafiyar Gaza.